An sake samun faruwar hatsarin jirgin ruwa a Yawuri
Rahotanni daga Jihar Kebbi a Najeriya sun tabbatar da sake samun wani mummunar hadarin jirgin ruwa a garin Yauri a yammacin ranar alhamis, kuma har zuwa wayewar gari wannan juuma’a ba’a san adadin wadanda suka rasa rayukansu sakamakon hadarin ba.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Kwanaki biyu da suka gabata ne wani hatsari makamancin wannan ya auku inda mutane kusan 20 suka mutu sakamakon kifewar kwale-kwalen da suke ciki.
Wani mazauni garin na Yauri Alhaji Dan Asabe Mai Fata Yawuri, ya ce har cikin daren jiya an ci gaba da bincike domin gano wadanda lamarin ya rutsa da su a wannan karo.
A Yawuri, kamar sauran garuruwa da ke yankin, jama’a na amfani jiragen ruwa ne domin gudanar da zirga-zirga da kuma sufuri sakamakon rashin gadoji.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu