APC ta ce rashin lafiyar Buhari kalubale ne ga manufofin jam'iyyar
Jam’iyyar APC a Najeriya ta ce rashin lafiya shugaban kasar Muhammadu Buhari lamari ne da ke haddasa tarnaki wajen aiwatar da manyan manufofin gwamnatin da ke kan karagar mulki.
Wallafawa ranar:
Bayan wata ganawa da suka yi da mukaddashin shugaban kasar Yemi Osinbajo a fadarsa da ke Abuja ranar laraba, shugabannin jam’iyyar a matakin jihohi, sun ce sun tattauna ne dangane da lamurran da suka shafi tafiyar kasar.
Henry Ajomale, shugaban jam’iyyar reshen jihar Lagos, ya ce ko shakka babu rashin lafiyar shugaban ya shafi tsari da kuma alkawurran da jam’iyyar ta yi a lokacin yakin neman zabe.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu