Yara 15 ne suka mutu bayan wata alura a Sudan ta kudu
Yara 15 ne aka bayyana mutuwar su bayan da aka yi masu alura ta yaki da kamuwa da cutar dusa mai dauke da guba a wani yanki mai suna Kapoeta na kasar Sudan ta kudu.
Wallafawa ranar:
Ministan kiwon lafiya na kasar ta Sudan ta kudu Riek Gai Kok a wata ganawa da manema labarai a Juba dake babban birnin kasar ya bayyana cewa binciken farko daga kwarraru tareda hadin guiwar ma’aikantan kiwo lafiya na hukumar lafiya ta Duniya na tabbatar da cewa an yi amfani da alura daya wajen yiwa ilahirin yara shau’shawa, banda haka babu kyaukiyawar kulawa dama tsapta a lokacin.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu