Angola
Ba zan nemi wani wa'adin ba- Jose Santos
Shugaban Angola Jose Eduardo dos Santos ya ce, ba zai nemi wani sabon wa’adi ba a zaben shugabancin kasar da za a gudanar a cikin wannan shekarar ta 2017.
Wallafawa ranar:
Talla
Wannan na zuwa ne bayan tsawon shekaru 38 da Santos ya shafe yana shugabancin Angola.
Yanzu haka dai, ministan tsaron kasar Joao Lourenco ne zai tsaya takarar shugabancin kasar a karkashin jam’iyyar MPLA mai mulki.
Ana saran gudanar da zaben a cikin watan Agusta mai zuwa.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu