Isa ga babban shafi
Ivory Coast

Sojoji na ci gaba da bore a Ivory Coast

Ana ta jin harbe-harbe da manyan bindigogi a manyan birane biyu na kasar Ivory Coast inda sojoji ke bore suna neman biyan su albashi mai tsoka da kuma basu gidan kwana don su mallaka. 

Shugaban kasar Ivory Coast Alassane Ouattara
Shugaban kasar Ivory Coast Alassane Ouattara Handout / IVORY COAST PRESIDENCY / AFP
Talla

Majiyoyi na cewa ana ta jin rugugin harsasan ne daga garuruwan Bouake gari na biyu mafi girma a kasar da kuma Korhogo.

Tun Juma'a sojojin suka kama garin Bouake inda suka dasa kansu a wasu muhimman wurare.

Cikin wata sanarwa Ministan Tsaro na kasar Alain-Richard Donwahi ya nemi sojojin da su yi hakuri domin Gwamnati na shirin sauraron koken su.

Boren ya yi sauya zuwa garuruwan Dalao, Daoukro da Odienne.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.