Ghana
Shugaban Majalisar Ghana ya yi watsi da bukatar 'yan adawa
Shugaban Majalisar kasar Ghana, ya yi watsi da bukatar 'yan adawar kasar na kaddamar da bincike kan kyautar da aka yiwa shugaban kasa John Dramani Mahama, dan niyyar tsige shi idan an tababtar da samun sa da laifi.
Wallafawa ranar:
Talla
'Yan adawar sun ce wani attajirin dan kasuwa daga kasar Burkina Faso Djibril Kanazoe ya samu aikin kwangila ne a kasar bayan ya baiwa shugaba Mahama wata motar alfarma.
Shugaban Majalisar Edward Adjaho yace zargin bashi da tushe.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu