Isa ga babban shafi
Sudan Ta Kudu

An kama bakin haure 816 a Sudan ta Kudu

Jami’an tsaro a kasar Sudan sun kama baki yan kasashen Afirka 816 akan iyakar kasar da Libiya wandanda ke kokarin tsallakawa nahiyar Turai cikin watanni biyu da suka gabata.

Masu neman ketarawa zuwa nahiyar Turai
Masu neman ketarawa zuwa nahiyar Turai RFI/Anthony Fouchard
Talla

Jami’an sun bayyana cewar 347 daga cikin su sun fito ne daga kasar Eritrea, 130 daga kasar Habasha yayinda 90 kuma yan kasar Sudan ne.

Mai Magana da yawun rundunar sojin kasar, Janar Aseer Hussein Bashir, yace sun rasa sojojin su guda biyu wajen fafatawa da masu safarar bakin, kuma sun kama 10 daga cikin su.

Matsalar safarar mutane zuwa nahiyar turai ta zama ruwan dare a nahiyar Afrika duk da kokarin da hukumomi ke yin a dakile hakan, abinda akafi dangatawa da talauci ke haifar da kara ta’azzarar matsalar.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.