Isa ga babban shafi
Najeriya

An bukaci a kafa dokar ta-baci a Borno saboda yunwa

Kungiyar Agaji ta Medecins Sans Frontieres ta bukaci Majalisar Dinkin Duniya ta kafa dokar ta-baci a yankin arewa maso gabashin Najeriya sakamakon matsalar yunwa da ake fama da ita. Kungiyar ta ce mutane da dama ne ke mutuwa sakamakon yunwa, yayin da wasu fiye da dubu 500 ke cikin matsanancin hali a yankin wanda Boko Haram ta daidaita.

Ana fama da yunwa a yankin arewa maso gabashin Najeriya
Ana fama da yunwa a yankin arewa maso gabashin Najeriya OCHA/Jaspreet Kindra
Talla

Rahoton na kungiyar likitocin MSF ya zo ne a daidai lokacin da tawagar kwamitin kula da ‘yan gudun hijira na majalisar wakilan kasar ya ziyarci garuruwan Damboa da kuma Bama, inda dubban mutane ke cikin matsanancin hali, Wakilin RFI Hausa a Maiduguri Bilyamin Yusuf ya ce Yara da dama ne suka mutu sakamakon cututtuka da yunwa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.