Isa ga babban shafi
Najeriya

Wata sabuwar kungiyar Niger Delta ta yi barazanar kai hare hare

Wata sabuwar kungiyar matasa da ke dauke da makamai a yankin Niger Delta mai arzikin mai a Najeriya da ke kiran kanta Joint Niger Delta Liberation Force, ta ce za ta kaddamar da hare-hare domin lalata kadarorin gwamnati  da aka gina da kudin mai na kasar, wanda kungiyar ta bayyana shi a matsayin arziki mallakin ‘yan yankin.

Sojojin Najeriya sun kaddamar da yaki akan tsagerun Niger Delta
Sojojin Najeriya sun kaddamar da yaki akan tsagerun Niger Delta REUTERS
Talla

Daga cikin wuraren da kungiyar ke shirin kai wa hari sun hada da fadar shugaban kasa da majalisun dokoki da ma’aikatun gwamnati da ginin kamfanin mai na NNPC, da babban bankin kasar da kuma barikokin soji.

Cikin sanarwar da kungiyar ta rabawa manema labarai tace za ta jefa gwamnati cikin kunci kamar yadda mutanen Niger Delta ke cikin kuncin rayuwa sakamakon gurbata muhallin yankin.

Wannan barazanar na zuwa ne bayan gwamnatin Muhammadu Buhari ta kaddamar da aikin tsabtace yankin Ogoni da tsiyayar mai ya lalata wa mutanen yankin muhallinsu.

Barnar da tsagerun Niger Delta suka aikata a bututun mai ya janyo wa Najeriya hasara, inda kasar ta koma fitar da danyen mai ganga 1.4 a rana maimakon ganga miliyan 2.2 a rana.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.