Kotun A Faransa Na Bincike Kaddarorin Wasu Shugabannin Africa
Alkalan wata kotu a kasar Faransa dake binciken tushen samun kudaden da aka sayi wasu tafka-tafkan gidaje na tsohon Shugaban Gabon Omar Bongo, sun bukaci a kwace kaddarorin daga hannun iyalan sa
Wallafawa ranar:
Majiyoyin sharia sun bayyana cewa Alkalan dake binciken na duba tulin wasu kaddarorin da Shugaban kasar Equitorial Guinea Teodoro Obiang ya mallaka tare da Shugaban kasar Congo Brazaville Dennis Sassaou Nguesso.
Tun cikin watan 12 na shekara ta 2010 aka fara binciken wadannan shugabannin Africa domin ganin ko kudaden haram ne suka yi amfani dashi wajen mallakan gidaje a Faransa.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu