Kasar Africa ta Kudu na Shirin Farfado da Jamiyyar ANC Sosai
Shugaban kasar Africa ta kudu Jacob Zuma ya kaddamar da manufofin babbar jamiyyar kasar ANC, a garin Port Elizabeth , inda ake ganin jamiyar na iya rasa yawan magoya baya a zaben da za’a gudanar watan Augusta mai zuwa.
Wallafawa ranar:
Gaza samun kuri'u masu yawa a wannan yanki na marigayi Uban kasar Nelson Mandela, zai zama abin kunya matuka ga Gwamnatin yanzu.
Shugaba Jacob Zuma ya fuskanci kiraye-kiraye na ya sauka dan tsakanin nan, tun bayan da wata kotu ta ce ya karya kundin tsarin mulkin kasar tunda yayi amfani da wasu makudan kudaden Gwamnati wajen gyatta gidan kansa.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu