Isa ga babban shafi
Libya

A maido da kudade don biyan bukatun marasa lafiya

Ministan lafiya na kasar Libya, na bangaren gwamnatin da kasashen duniya suka yi na’am dasu, ya nemi Majalisar Dinkin Duniya da ta bari su yi amfani da kudaden kasar da aka boye a asusun bankuna a wajen kasar

Mata da yara a zanga-zangar juyin juya hali a Libya
Mata da yara a zanga-zangar juyin juya hali a Libya Reuters路透社
Talla

Ministan lafiya Redha El-Oakley ya shedawa manema labarai a Ofishin Majalisar Dinkin Duniya dake Tunis, cewar abin babu dadi yadda kasar ke fama da matsalar rashin kudi da zata sayo magunguna don baiwa dimbin marasa lafiya, duk da cewa akwai kudaden ta masu yawa da aka hanata dake waje.

A kasar Tunisia kawai inji shi, akwai kudin kasar dala Miliyan 295 da aka rufe, kuma shekara daya kenan suna ta zarya zuwa Tunis amma samun kudaden ya faskara.

Libya ta fada cikin rikici ne a shekara ta 2011 a lokacin da aka kawo karshen mulkin marigayi shugaba Moammar Ghadafi

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.