Isa ga babban shafi
Afrika

Afrika ta kudu na kan gaba a cin hanci da rashawa

Kungiyar da ke yaki da cin hanci da rashawa a duniya ta Transparency International ta ce kasar Afirka ta kudu ta fi kowacce kasa a Afirka samun karuwar cin hanci da rashawa a cikin watanni 12 da suka wuce.

Afrika ta kudu na kan gaba a cin hanci da rashawa a Afrika
Afrika ta kudu na kan gaba a cin hanci da rashawa a Afrika @បណ្តាញសង្គម
Talla

Rahotan ya ce a karon farko ana samun mutanen da ke fitowa fili suna karar jami’an gwamnati a kasashensu da ke bukata ko karbar cin hanci da rashawa.

A cikin kasashe 18 daga cikin 28 da aka gudanar da bincike akan su a Afirka, akasarin mutanen da aka tuntuba sun bayyana cewar gwamnatocin su basa daukan matakan da suka dace domin magance matsalar.

Binciken ya nuna cewar an samu karuwar cin hanci a kasashen Saliyo da Najeriya da Liberia da kuma Ghana, yayin da aka samu raguwarsa a kasashen Botswana da Burkina Faso da Lesotho da kuma Senegal.

Kungiyar ta ce ta tuntubi mutane 43,143 a kasashe 28 kafin fitar da rahotan ta.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.