Isa ga babban shafi
Angola

An kama masu yi wa 'yan adawa addu'a a Angola

'Yan Sanda a kasar Angola sun kama mutane 20 da suka kwashe dare suna addu’a ga 'yan adawar da aka tsare cikin su har da wani fitaccen mawaki Luaty Beirao, wanda aka tsare tun watan Yuni.

Jami'an 'Yan Sanda a Luanda na kasar Angola.
Jami'an 'Yan Sanda a Luanda na kasar Angola. AFP PHOTO/ESTELLE MAUSSION
Talla

Rahotanni sun ce akalla mutane 100 suka taru a wata Mujami’a da ke Luanda domin addu’ar ganin an saki mutanen 15 da aka tsare, saboda zargin da ake musu na yunkurin kifar da gwamnati.

Su dai mutanen na bukatar ganin shugaban kasar Jose Eduardo Dos Santos wanda ke karagar mulki tun shekarar 1979 ya sauka daga mukaminsa ne.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.