Isa ga babban shafi
Jamhuriyar Demokradiyar Congo

Jam’iyyar adawa ta janye daga tattaunawa da Kabila

Babbar Jam’iyyar adawar kasar Jamhuriyar Demokiradiyar Congo ta sanar da ficewa daga tattaunawar da ta ke da wakilan shugaban kasar Joseph Kabila kan shirin zaben shugaban kasar da za a yi a shekara mai zuwa.

Shugaban Jamhuriyyar Congo Joseph Kabila,
Shugaban Jamhuriyyar Congo Joseph Kabila, AFP PHOTO / CARL DE SOUZA
Talla

Wakilan bangarorin biyu na ganawa ne a Turai don tattauna yadda za a gudanar da zabe cikin kwanciyar hankali a watan Nuwamba na shekarar 2016.

Ma su sa ido na zargin shugaba Joseph Kabila da yunkurin tsawaita mulkinsa idan wa’adinsa na biyu ya kawo karshe shekara mai zuwa.

Wakilan Jam’iyyar UDPS ta madugun adawa Etienne Tshisekedi na tattaunawa da wakilan gwamnatin Kabila ne a Brussels, kuma a ranar Lahadi ne bangaren jam’iyyar adawar ta fitar da sanarwar ficewa daga zauren tattaunawar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.