Sojoji sun fatattaki Boko Haram da ke kokarin kutsawa cikin Maiduguri
A cikin daren juma’ar da ta gabata, wasu da ake zaton cewa magoya bayan kungiyar Boko haram ne sun share tsawon sa’o’i akalla biyu suna fafatawa da dakarun gwamnatin Najeriya a wani wuri da ke wajen birnin Maiduguri na jihar Borno.
Wallafawa ranar:
Shaidu sun ce wasu ‘yan bindiga ne suka yi kokarin mamaye kauyen Zabarmari mai tazarar kilomita 10 daga Maiduguri, to sai dai sojojin na gwmanatin sun yi nasarar fatatakarsu.
A cikin kwanaki biyu da suka gabata, hare-haren da ake dangantawa da kungiyar ta Boko Haram sun yi sanadiyyar mutuwar sama da mutane 200 a sassa daban daban na jihar ta Borno.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu