Isa ga babban shafi
Afrika

Kungiyar Ecowas ta bukaci a dage zabe a Togo

Kungiyar Kasashen Afrika ta Yamma wato ECOWAS ta bukaci jinkirta gudanar da zaben shugaban kasar Togo saboda abinda ta kira korafe korafen yan adawa wajen rubuta sabon rajistar masu kada kuri’u.Ana cigaba da samu tashe-tashen hankula a wasu biranen kasar, yayi da yan adawa ke cigaba da yi kira zuwa Shugaban kasar Faure Gnassigbe da ya kaucewa sake neman kujerar shugabancin  kasar ta Togo.

Wasu masu zanga zangar a birni Lome na kasar Togo
Wasu masu zanga zangar a birni Lome na kasar Togo FP PHOTO/ EMILE KOUTON
Talla

Shugaban Kasar Ghana John Dramani Mahama dake shugabancin kungiyar ya bayyana haka lokacin da ya ziyarci kasar Togo.

Kungiyoyin fararen hula  a kasar dama wasu daga cikin yan siyasa na fatar gani hukumar zabe ta yi naam da wanan bukata daga  kungiyar kasashen  Afrika ta yama Ecowas.

Hakan kuma wata hanyar ceto kasar ta Togo  daga fadawa cikin wani sabon rikicin siyasa inji Shugaban kasar Ghana kuma  Shugaban kungiyar Ecowas.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.