WHO: Ebola ta kashe mutane 10,000
Hukumar Lafiya ta Duniya WHO ta bayyana cewa zuwa yanzu fiye da mutane 10,000 ne suka mutu cikin mutane 24,000 da suka kamu da cutar cutar Ebola, a kasashen yammacin Afrika. Cutar ta fi yin kisa a kasashen Liberia da Saliyo da Guinea.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Wasu 6 sun mutu a Mali, guda a Amurka yayin da 8 suka rasa ransu a Najeriya, inda aka yi hanzarin kawar da cutar.
Rahoton hukumar ya ce akwai mutum guda mai dauke da cutar a Senegal da Spain, amma babu rahoton mutuwa a kasashen.
A kasar Saliyo an bayyana cewa adadin mutane 11,677 suka mutu, a Liberia kuma 3,655, a Guinea mutane 2,187 suka mutu.
Amma a makon jiya ne kasar Liberia ta bayyana sallamar mutum na karshe da ake kula da shi a Asibiti bayan gwaji ya nuna ba ya dauke da Ebola.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu