An kashe 'Yan Boko Haram a Kamaru
Mayakan Boko haram na Najeriya sun kai hari a garin Karewa da ke kan iyaka da Kamaru, inda rahotanni suka ce an kwashe sa’o’I ana ruwan wuta tsakanin Mayakan da Sojoji Lamarin kuma ya yi sanadin mutuwar Mayakan na boko Haram da dama da kuma Soja guda.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Rahotanni daga Najeriya na cewa Mayakan Boko Haram sun kama garin Malam Fatori a Jihar Borno da ke dab da kan iyaka da Jamhuriyyar Nijar.
Mahukuntan Diffa sun ce Sojoji sama da 300 ne suka samu mafaka a Jihar diffa bayan da Mayakan Boko Haram suka fatttakesu .
Kuma akwai Sojoji kusan 13 kwance a gadon Asibiti.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu