Isa ga babban shafi
Afrika ta Tsakiya

An kashe wata ‘Yar Jaridar Faransa a Afrika ta tsakiya

An kashe wata ‘Yar Jaridar kasar Faransa mai daukar hoto a wani harin kwantar bauna yayin da ta ke gudanar da aikinta a kasar Jamhuriyyar Afrika ta tsakiya mai fama da rikicin addini. Fadar shugaban kasar Faransa tace wasu dakarun wanzar da zaman lafiya ne suka tsinci gawar Camille Lepage a cikin wata mota da wasu mayakan Anti Balaka ke ciki a yankin Bour da ke Yammacin kasar.

'Yar Jaridar kasar Faransa Camille Lepage da aka kashe a Afrika ta tsakiya
'Yar Jaridar kasar Faransa Camille Lepage da aka kashe a Afrika ta tsakiya AFP / FRED DUFOUR
Talla

Kisan Lepage na zuwa ne duka watanni shida da aka kashe wani dan jarida a kasar Mali.

Kwamitin tsaro na Majalisar Dinkin Duniya ya yi Allah waddai da kisan ‘Yar Jaridar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.