Sabuwar kungiyar ‘Yan tawayen Mali za ta halarci taron samar da zaman lafiya
Wata sabuwar kungiyar ‘Yan tawayen Larabawan a kasar kasar Mali, ta ce za ta halarci tattaunawar samar da zaman lafiya da ake shirin gudanarwa a cikin watan Yuli mai zuwa tsakanin gwamnatin kasar da kuma sauran kungiyoyin ‘yan tawaye a karkashin jagorancin shugaban kasar Burkina Faso Blaise Compaore.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Kungiyar mai suna MAA, ta gana da manzon na musamman da gwamnatin Mali ta tura zuwa birnin Nouackshot na kasar Mauritaniya, Tiebile Drame a marecen jiya Alhamis,
Haka kuma kungiyar ta bayar da tabbacin cewa za ta shiga tattaunawa da za a buda a ranar 28 ga watan Yuli, wato a daidai lokacin da ake shirin gudanar da zaben shugabancin kasar.
A daya bangare kuwa kasar Sweden, ta yi alkawarin aikewa da dakarunta 70 domin shiga rundunar wanzar da zaman lafiya da ke aiki a kasar ta Mali,
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu