Isa ga babban shafi
Mali

Sabuwar kungiyar ‘Yan tawayen Mali za ta halarci taron samar da zaman lafiya

Wata sabuwar kungiyar ‘Yan tawayen Larabawan a kasar kasar Mali, ta ce za ta halarci tattaunawar samar da zaman lafiya da ake shirin gudanarwa a cikin watan Yuli mai zuwa tsakanin gwamnatin kasar da kuma sauran kungiyoyin ‘yan tawaye a karkashin jagorancin shugaban kasar Burkina Faso Blaise Compaore.

Wasu dakarun wanzar da zaman lafiya a kasar Mali
Wasu dakarun wanzar da zaman lafiya a kasar Mali Reuters
Talla

Kungiyar mai suna MAA, ta gana da manzon na musamman da gwamnatin Mali ta tura zuwa birnin Nouackshot na kasar Mauritaniya, Tiebile Drame a marecen jiya Alhamis, 

Haka kuma kungiyar ta bayar da tabbacin cewa za ta shiga tattaunawa da za a buda a ranar 28 ga watan Yuli, wato a daidai lokacin da ake shirin gudanar da zaben shugabancin kasar.

A daya bangare kuwa kasar Sweden, ta yi alkawarin aikewa da dakarunta 70 domin shiga rundunar wanzar da zaman lafiya da ke aiki a kasar ta Mali,
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.