Cote d'Ivoire
Ana gudanar da zaben kananan hukumomi a Cote D'Ivoire
A yau lahadi 21 ga watan Afrilu ana gudanar da zaben ‘yan majalisun kananan hukumomi da na manyan yankunan a kasar Cote D’Ivoire.
Wallafawa ranar:
Talla
Tuni dai magoya bayan jam’iyyar FPI ta tsohon shugaban kasar Laurent Gbgabo sun yi watsi da shiga wannan zabe na yau.
Yakin neman zaben dai ya kawo karshensa a ranar juma’ar da ta gabata, a dan takaitacen yankin neman zabe da ya gudana cikin wani irin yanayi na fargaba.
An dai buda rumfunan zabe ne da misalin karfe 7:30 na safen agogon kasar yayin da ake jiran sakamakon zaben a tsakiyar makon gabe.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu