Isa ga babban shafi
Jamhuriyar Afrika ta Tsakiya

Bozize ya zargi kasar Chadi da taimakawa ‘Yan tawayen da suka hambarar da gwamnatin shi

Hambararren shugaban kasar Jamhuriyyar Afrika ta Tsakiyar, Francois Bozize ya yi zargin cewa kasar Chad ice ta taimakwa ‘Yan tawayen Seleka suka hambarar da gwamnatin shi kamar yadda A cewar rahotanni suka nuna.

Shugaban kasar Jamhuriyar Afrika ta Tsakiya, Francois Bozize
Shugaban kasar Jamhuriyar Afrika ta Tsakiya, Francois Bozize REUTERS/Luc Gnago
Talla

A cewar shi, kamin hambarar da gwamnatin ta shi, dakarun kasar sun samu nasara akan ‘Yan kungiyar ta Seleka.

‘‘Mun samu galaba akan dakarun Seleka a ranar Assabar amma kuma daga baya mun san akwai taimako da suka samu daga wata kasar Afrika kuma na yi imanin kasar Chadi ce.’’ Inji Bozize

Wannan dai shine karo na farko da Bozize ya fito ya yi magana a kafar yada labarai tun bayan hambarar da gwamnatin shi.

Gwamnatin Chadi dai ta taka muhimmiyar rawa wajen taimakwa Bozize a shekarun day a kwashe yana shugabanci a kasar tare da taimaka masa hambarar da gwamnatin kasar a shekarar 2003.

Izuwa hada wannan rahoto gwamnatin ta Chadi ba ta mayar da martani akan wannan zargi na Bozize ba.

 

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.