Isa ga babban shafi
Kenya

Lauyoyin Kenyatta sun bukaci a janye tuhumar da ake yi masa

Lauyoyin zababben shugaban kasar Kenya Uhuru Kenyatta sun bukaci kotun hukunta laifukan yaki ta Duniya wato ICC da ta jingine tuhumar da take wa Uhuru Kenyatta, dangane da tashin hankalin siyasa da ya faru a shekarar 2007. Daya daga cikin Lauyoyin, Kenyatta, Steven Kay ya bukaci Alkalan Kotun su 3 da su cire Kenyatta daga karar da za’a shigar a watan Yuli.  

Zababben shugaban kasar Kenya, Uhuru Kenyatta
Zababben shugaban kasar Kenya, Uhuru Kenyatta REUTERS/Marko Djurica
Talla

A cewarsa an gurgunta shaidun da aka gabatar kan zargin da aka yiwa Francis Muthaura wanda aka zarga tare da Kenyatta ne ta hanyar cire daya daga cikin shaidu masu muhimmanci.

Ya kara da cewa ya kamata a duba al’amari shi Uhuru Kenyatta ta hanyar sake duba zargin da ake masa da suka hada da fyade, da kisa.

 

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.