Isa ga babban shafi
Libya

An zabi sabon Fira Minista a Libya

Gwamnatin wuccin gadi a kasar Libya, ta zabi Abdurahim al Kib, a matsayin wanda zai jagoranci Gwamnatin rikon kwarya, yayin da kungiyar kawancen tsaro ta NATO, ta kawo karshen yakinta a cikin kasar.Al Keib, wanda kwararen injiniya ne a fannin lantarki, ya fito ne daga Tripoli, kuma ya kada abokan takararsa hudu, da kuri’a 26 daga 51 da aka kada.Shugaban rikon kwarya, Mustafa Abdul Jalil, ya bayyana zaben shi a matsayin wani tabbaci cewar ‘Yan kasar Libya na iya gina makomarsu.Keib wanda malamin Jami’a ne kuma dan kasuwa, ya kwashe shekaru a kasashen waje wanda ya dade yana adawa da gwamnatin Muammar Gaddafi.Tun kafin zabensa kungiyar NATO ta bayyana kawo karshen yakinta a kasar Libya inda shugaban kungiyar Anders Fogh Rasmussen yace babu wata rawa da zasu taka bayan kawo karshen Gaddafi.    

Shugaban NTC Mustapha Abdeljalil, da Sabon Fira Minista Abdurrahim Keib
Shugaban NTC Mustapha Abdeljalil, da Sabon Fira Minista Abdurrahim Keib
Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.