Nijar
A Nijar an nada sabin mambobin gwamnatin jumhuriya ta 7
A jumhuriyar Nijar,bayan rantsar da Praministan kasar yau a zauren majalasar dokokin kasar,an kuma nada sabin mambobi na sabuwar gwamnati ta farko a jumhuriya ta 7.Gwamnatin da ta kumshi mambobi 24 ,mata 6 a ciki.Da ga cikin mambobin wanan sabuwar gwamnati ,a koye Malam Bazoum Mohamed da ke rike da ma’aikatar harkoki, da hulda da kasashen waje, Amadou Boubakar Cisse ma’aikatar fassali, Abdou Labo na jama’iyar CDS-Rahama ma’aikatar cikin gida, Marou Amadou tsohon shugaban majalasar tuntubar juna a ma’aikatar shara’a kuma kakakin gwamnati.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar: