Isa ga babban shafi
Niger

Amurika ta janye yan kasar ta masu yin hidimar kasa a kasar Nijar

Kasar Amurika ta kwashe ‘yan kasar ta guda 98 masu hidimar kasar a kasar jumhuriyar Nijar.Kasar Amurika ta yi haka ne, sabili da abun da ta kira tabarbarewar lamuren tsaro a cikin kasa. Tun dai lokacin da kungiyar Al’kaida,a yankin yammaci Afrika ta sace ‘yan kasar Franshinan guda 2,da kuma su ka tarda ajalin su a cikin fafatawar da ta wakana, tsakanin ‘yan kungiyar da dakarun kasar Franshi a cikin wani yanki na kasar Mali ,dokacin masu fata da fari,’yan kasashen turai da na yammacin ta, su ka tsamtsamta da kasar ta Nijar.Tun dai cikin shekara ta 1962,shekara 2 kenan bayan samun incin kan kasar ta Nijar ne kasar Amurika ta girka wanan tsari na turo’yan kasar ta,domin yin hidima ga kasar Nijar. 

Jami'an tsaro na sunturi
Jami'an tsaro na sunturi RFI/Julie Vandal
Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.