Isa ga babban shafi
Najeriya

Najeriya: Mutane 37 aka kashe a harin Adamawa

Akalla mutane 37 suka mutu a hare haren da ‘Yan bindiga da ake kyautata zaton Mayakan Kungiyar Boko Haram ne suka kai a Jahar Adamawa, kamar yadda Jami’an gwamnati da mazauna garuruwan da aka kai hare haren suka tabbatar.

Familles de Gwoza, dans l'Etat de Brono, déplacées par la guerre contre Boko Haram, en février 2014.
Familles de Gwoza, dans l'Etat de Brono, déplacées par la guerre contre Boko Haram, en février 2014. REUTERS/stringer
Talla

Shugaban karamar hukumar Madagali a Jahar Adamawa, Maina Ularamu yace an kai jerin hare hare ne guda uku ne a Shuwa da Kirchinga da Michika.

“‘Yan bindigan sun raba kansu ne gida uku” kamar yadda ya shaidawa Kamfanin Dillacin Labaran Faransa.

Ularamu yace a garin Shuwa mutane 25 ne aka kashe bayan an gano gawawwakin mutane takwas a wata makarantar mabiya Addinin Kirista.

Rahotanni sun ce dukkanin ‘Yan bindigan sun yi shiga ne sanye da kakin Soja a hare haren da suka kai.

Tun da farko dai, Jami’an tsaro sun tabbatar da hare haren da aka kai a Adamawa amma sun ce Soja guda ne aka kashe da wasu fararen hula guda uku.

Jahar Adamawa dai tana cikin Jahohi uku a yankin arewa maso gabaci da aka kafawa dokar ta-baci, kuma tun daga farkon shekara ta 2014 zuwa yanzu akalla mutane 300 suka mutu a hare haren da aka kai a Jahohin Borno da Yobe da Adamawa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.