Nigeria Tayi Shekaru 18 Da Zaben Abiola
Yau aka cika shekaru 18 a Nigeria da soke zaben da aka hakikance da cewa hamshakin Attajiri Chief Mashood Abiola ne ya lashe, amma aka soke.Gwamnatin Janar Ibrahim Badamasi Babangida ce ta soke zaben, saboda wasu dalilai da har ya zuwa wannan lokaci babu wanda zai iya fadin takamaiman dalili.Wasu jihohin yankin da marigayi Chif Abiola ya fito sun ware yau da gobe littini amatsayin ranar hutu domin girmama wannan rana.Tun bayan mutuwar Abiola Nigeria ta sami Shuagabanni shida ya zuwa wannan lokaci.Sun hada da Cif Earnest Shonekan, Marigayi Sani Abatcha, Gen Abdulsalam Abubakar, Cif Olusegun Obasanjo, Marigayi Umaru Musa ‘Yaraduwa da kuma Dr Goodluck Jonathan.
Wallafawa ranar: