A baya, an san mata da gudanar da harkokin gida ne kawai yayinda su kuma mazajensu, kan fita waje domin neman abin rufin asirin iyali. A cikin wannan shiri, mun duba yadda ake samun karuwar mata dake shiga cikin harkokin noma, sannan mun duba yadda mata manoma, ke samun tallafi daga cibiyoyin bada tallafin noma domin bunkasa harkarsu ta noma. Bugu da kari, wani tasiri noman mata ke yi ga gudanar da harkokin gidajensu.Hakanan wannan shiri, yana karfafa guiwar mata ne domin su rungumi harkar noma, kiwo da dangoginsu gadan gadan, musamman yanzu da ake da cibiyoyin dake tallafa musu.
Sauran kashi-kashi
-
Najeriya ta kasance kan gaba a fagen noman masara a yankin yammacin Afrika
Shirin wannan mako zai ba da hankali ne a kan yadda Najeriya ta kasance akan gaba a fagen noman masara a daukacin yankin yammacin Afrika, inda kasar ke samar da sama da kashi 48 na masarar da ake nomawa a yankin.Mafi yawan masarar da ake nomawa a kasar, na fitowa ne daga yankin arewacin kasar, musamman jihohin Bauchi, Kaduna, Borno, Naija da Taraba da kuma wasu ‘yan kalilan din jihohin kudu maso yammacin kasar.23/03/202421:02 -
Yadda wasu suka rungumi sana'ar kiwon Dodon kodi a yankin Naja Delta
Shirin mu na wannan mako zai yi duba ne a kan batun yadda wasu suka rungumi sana'ar kiwon Dodon kodi a yankin Naja Delta da ke tarayyar Najeriya musamman a jahar Cross River.Wakilin mu dake yankin MURTALA ADAMU ya kai ziyara a wa ta Gona da ake wannan kiwon kuma ya zanta da wadanda suke sana'ar, wa ta da ta rungumi sana'ar ta yi bayani dalla dalla yadda ake fara tsara kiwon da kuma abubuwa da suka dace a tanada.24/02/202417:26 -
Halin da yankunan da suka gamu da iftila’in ambaliya ke ciki a Najeriya
Shirin awannan mako zai maida hankali ne kan batun halin da yankunan da suka gamu da iftila’in ambaliya ke ciki a Najeriya, tare da duba matakan da suke dauka na kare kai anan gaba.Idan ba a manta ba dai Shekara guda kenan da faruwa mummunar ambiyar ruwa a wasu jihohin Najeriya, kuma jihar jigawa dake arewacin kasar na cikin jihohin da ambaliyar tayiwa barna10/02/202420:09 -
Gwamnatin Najeriya ta kudiri aniyar amfani da noman alkama don samar da aikin yi
A wannan mako shirin zai yi dubi ne akan shirin gwamnatin Najeriya na bunkasa noman alkama domin yaki da talauci da kuma wadata kasar da abinci.A wani mataki na kawar da matsalar zaman kashe wando da magance rashin aikin yi musamman tsakanin matasa, gwamnatin Nigeria ta kuduri aniyar amfani da noma wajen samar da guraben aikin yi wa dubban matasan da basa da abin yi a fadin kasar.29/01/202419:28 -
Hasarar da manoma suka samu a yayin girbin kayayyakin da suka noma a Najeriya
Hasarar da manoma suka samu a yayin girbin kayayyakin da suka noma a Najeriya wadda gwamnatin kasar tace yakan kai sama da Nera triliya 3 a kowacce shekara .Sashen Hausa na Radio France International ya yi tattaki zuwa jihar Kano a Najeriya inda muka gana da masu ruwa da tsaki domin jin yadda ta kaya a wannan karowandada suka kuma bayyana cewa anfi samun asarar mafi girma akan kayan lambu amma hakan bai tsaya a bangare guda ba domin hatsi ma ba a barshi a baya ba20/01/202420:59