Chanjin yanayi ko dumamar sa, batu ne dake cigaba da haddasa zazzafar muhawara da musayar ra'ayi tsakanin masana da kwararraru,musamman kan illolin da wannan batun zai haifar a rayuwar bil adama a doron kasa. Tuni dai wani taron kasa-da-kasa a birnin Copenhegen na Denmark,yayi kasedi cewa dole kowacce kasa ta tanadi yadda zata tunkari wannan batu na chanji yanayi daya fara bayyana a ambaliyar ruwan sama da kuma karancin sa a wani bangare na duniya bisa wasu dalilai.Sai dai kuma kamar yadda bincike ya nuna a Nigeria kamar sauran kasashe masu tasowa inda wannan matsala ta chanji yanayi tafi bayyana,galibin jama'a basu san wannan batu ba,balle ma suyi la'akarin yadda zasu bullo masa. Wannan jahilcin dake bayyana game da batun na chanjin yanayi,yasa al'umma na cigaba da gurbata muhalli ba tare da sanin illolin da wannan gurbatar ke haifarwa ba.Watakila dai chunkoson abubuwan hawa a birane dake fitar da gubataccen iska/hayaki da kuma musamman sarar itatuwa a matsayin makamashi,sune kan gaba wajen haifar da matsalolin gusowar hamada,zaizayar kasa da kuma yanayin dake barazana ga tsirrai ko yabanya. Wadannan sune mayan kalubalen da galibin kasashe masu tasowa ke fuskanta,kalubalen samun makamashi mai sauki domin rage chi iyakar da kullu yaumin ake wa dazuzzuka wajen neman itace girki.A yayin da hukumomi musamman a Nigeria ke dawainiyar binciken wasu hanyoyi na samun makamashi mafi sauki da arha,bincike ya nuna cewa sana'ar itace da yin gawayi,na cigaba da bunkasa a yawanci jihohi da kananan hukumomi duk kuwa da cewa akwai dokar dake tsawatawa kan haka.
Sauran kashi-kashi
-
Najeriya ta kasance kan gaba a fagen noman masara a yankin yammacin Afrika
Shirin wannan mako zai ba da hankali ne a kan yadda Najeriya ta kasance akan gaba a fagen noman masara a daukacin yankin yammacin Afrika, inda kasar ke samar da sama da kashi 48 na masarar da ake nomawa a yankin.Mafi yawan masarar da ake nomawa a kasar, na fitowa ne daga yankin arewacin kasar, musamman jihohin Bauchi, Kaduna, Borno, Naija da Taraba da kuma wasu ‘yan kalilan din jihohin kudu maso yammacin kasar.23/03/202421:02 -
Yadda wasu suka rungumi sana'ar kiwon Dodon kodi a yankin Naja Delta
Shirin mu na wannan mako zai yi duba ne a kan batun yadda wasu suka rungumi sana'ar kiwon Dodon kodi a yankin Naja Delta da ke tarayyar Najeriya musamman a jahar Cross River.Wakilin mu dake yankin MURTALA ADAMU ya kai ziyara a wa ta Gona da ake wannan kiwon kuma ya zanta da wadanda suke sana'ar, wa ta da ta rungumi sana'ar ta yi bayani dalla dalla yadda ake fara tsara kiwon da kuma abubuwa da suka dace a tanada.24/02/202417:26 -
Halin da yankunan da suka gamu da iftila’in ambaliya ke ciki a Najeriya
Shirin awannan mako zai maida hankali ne kan batun halin da yankunan da suka gamu da iftila’in ambaliya ke ciki a Najeriya, tare da duba matakan da suke dauka na kare kai anan gaba.Idan ba a manta ba dai Shekara guda kenan da faruwa mummunar ambiyar ruwa a wasu jihohin Najeriya, kuma jihar jigawa dake arewacin kasar na cikin jihohin da ambaliyar tayiwa barna10/02/202420:09 -
Gwamnatin Najeriya ta kudiri aniyar amfani da noman alkama don samar da aikin yi
A wannan mako shirin zai yi dubi ne akan shirin gwamnatin Najeriya na bunkasa noman alkama domin yaki da talauci da kuma wadata kasar da abinci.A wani mataki na kawar da matsalar zaman kashe wando da magance rashin aikin yi musamman tsakanin matasa, gwamnatin Nigeria ta kuduri aniyar amfani da noma wajen samar da guraben aikin yi wa dubban matasan da basa da abin yi a fadin kasar.29/01/202419:28 -
Hasarar da manoma suka samu a yayin girbin kayayyakin da suka noma a Najeriya
Hasarar da manoma suka samu a yayin girbin kayayyakin da suka noma a Najeriya wadda gwamnatin kasar tace yakan kai sama da Nera triliya 3 a kowacce shekara .Sashen Hausa na Radio France International ya yi tattaki zuwa jihar Kano a Najeriya inda muka gana da masu ruwa da tsaki domin jin yadda ta kaya a wannan karowandada suka kuma bayyana cewa anfi samun asarar mafi girma akan kayan lambu amma hakan bai tsaya a bangare guda ba domin hatsi ma ba a barshi a baya ba20/01/202420:59