Wasanni
Fifa na nazarin yiyuwar kara yawan kasashen da ke shiga gasar kofin duniya
Wallafawa ranar:
Kunna - 09:58
Yanzu haka hukumar kwallo kafa ta duniya FIFA ta fara nazarin yiyuwar kara yawan kasashen da za su shiga gasar neman kofin duniya. Shugaban hukumar Gianni Infantino ne ya sanar da wannan aniya.A cikin shirin Duniyar Wasanni na wannan mako, Ahmed Abba ya yi dubi a game da wannan yunkuri.