A farkon wannan mako ne aka gudanar da zaben shugaban kasa, zagaye na biyu a kasar Senegal, tsakanin shugaba Abdoulaye Wade, wanda ke rike da karagar mulki da Macky Sall, shugaban ‘Yan adawar kasar. Tuni sakamakon zaben ya nuna cewa, shugaba Wade ya sha kaye, yayin da Macky Sall da ya samu goyan bayan sauran ‘Yan takaran, ya zama zababben shugaban kasa.