Isa ga babban shafi
Iran-Turai

Turai ta zargi Iran da kai hari Saudiya

Shugabanin Kasashen Turai da suka hada da na Faransa da Jamus da kuma Birtaniya sun bayyana cewar Iran ce ta kai hari cibiyar samar da man Saudi Arabia, inda suka bukaci kasar ta dauki matakan diflomasiya domin warware matsalolin ta maimakon takalar fada.

Shugaban Faransa  Emmanuel Macron, da waziriyar Jamus Angela Merkel da Borris Johnson na Birtaniya
Shugaban Faransa Emmanuel Macron, da waziriyar Jamus Angela Merkel da Borris Johnson na Birtaniya REUTERS/Philippe Wojazer/Pool
Talla

Shugaba Emmanuel Macron da Angela Merkel da Boris Johnson sun bayyana karara cewar ya zama wajibi Iran ta dauki alhakin kai harin a sanarwar hadin gwuiwa da suka bayar a Majalisar dinkin Duniya, inda suke cewa suna goyan bayan daukan matakan diflomasiya wajen magance matsalar.

Shugabannin sun kuma bukaci Iran ta koma mutunta yarjejeniyar nukiliyar da suka kulla a shekarar 2015.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.