Jawabin Farfesa Umar Garba Dambatta wakilin Najeriya a taron bajekolin fasahar sadarwa ta duniya a Budapest
Wallafawa ranar:
Kunna - 03:51
Gobe ake kamala taron baje kolin fasahar sadarwa ta duniya, wadda ke janyo hukumomin sadarwa daga sassan duniya da kuma kamfanonin da ke kera kayyakin da ake aiki da su da masana fannin, wadanda ke bajekoli da kuma musayar ra’ayi kan cigaban da ake samu a duniya.Taron na bana ya mayar da hankali ne kan batun hanyar sadarwar da ake kira 5G wanda tuni kasashen da suka cigaba ke rige rige wajen inganat hanyoyin sadarwar su da shi.Mun tattauna da Farfesa Umar Garba Dambatta, shugaban hukumar sadarwar Najeriya da yanzu haka ke Budapest inda ake gudanar da taron, inda na fara tambayar sa kan abinda taron ya mayar da hankali akai, sai ya kada baki yace.