Isa ga babban shafi

Javad Zarif na Iran ya yiwa taron G7 shigar bazata a Faransa

Babban Jami’in Diflomasiyyar Iran kuma ministan harkokin wajen kasar Mohamed Javad Zarif ya yiwa taron G7 can a birnin Biarritz na Faransa shigar bazata, matakin da ke nufin samar da daidaito kan tsamin alakar da ke kara tsami tsakanin Tehran da Amurka.

Ministan harkokin wajen kasar Iran, Mohammad Javad Zarif.
Ministan harkokin wajen kasar Iran, Mohammad Javad Zarif. NTB Scanpix/Stian Lysberg Solum/ via REUTERS
Talla

Mohamed Javad Zarif wanda ke fuskantar takunkuman Amurka ya yiwa taron na G7 shigar bazata a jiya Lahadi bisa gayyatar shugaba Emmanuel Macron ko da dai Donald Trump ya ce ya na da cikakkiyar masaniya kan zuwansa, hasalima sai da Macron ya nemi shawararsa kafin aikewa Iran da goron gayyatar.

Gabanin barinsa birnin Biarritz na Faransa, Javad Zarif ya yi tattaunawar akalla sa’o’I 3 da shugaba Emmannuel Macron gabanin komawa Tehran.

Ka zalika yayin jawabinsa gaban wakilan Turai da suka kunshi wakilan kasashen Jamus Birtaniya da kuma Faransa, Javad Zarif ya ce batun tattaunawarsu da Amurka batu ne mai cike da sarkakiya da kuma wahala amma suna bukatar gwadawa.

Sai dai cikin kalaman Donald Trump bayan halartar Zarif Faransa, ya ce lokaci ya yi wuri su fara tattaunawa da Iran yana mai cewa basu matsu a fita daga halin da ake ciki yanzu haka ba.

Shugabannin Turai dai karkashin jagorancin Macron na ci gaba da kai ruwa rana wajen ganin an sulhunta rikicin tsakanin Amurka da Iran.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.