Isa ga babban shafi

Dan bindiga ya kashe masu siyayya 20 a jihar Texas ta Amurka

Akalla mutane 20 aka tabbatar da mutuwarsu bayan harin dan bindigan da ya bude wuta kan masu siyayya a wani shagon zamani da ke yankin El Paso na jihar Texas a Amurka. Harin wanda ya faru a jiya Asabar tuni aka fara alakanta shi da na nuna kyama.

Wasu tarin jami'an tsaro da aka aike yankin na El Paso a jihar Texas yayin faruwar harin a jiya Asabar
Wasu tarin jami'an tsaro da aka aike yankin na El Paso a jihar Texas yayin faruwar harin a jiya Asabar Joel Angel JUAREZ / AFP
Talla

Tuni dai Jami'an 'yan sanda suka kame mutumin da ya kaddamar da harin yayinda suka ce za a fara yi masa tuhuma.

Harin wanda shi ne na baya-bayan nan da aka kaddamar a kasar ta Amurka mai fama da matsalar hare-haren ‘yan bindiga wanda ke da nasaba da nuna wariya ko kuma kyama ya kuma jikkata mutane 26.

Tuni dai shugaban kasar ta Amurka Donald Trump da gwamnan jihar ta Texas suka yi tir da harin yayinda jami’an tsaro suka ce suna ci gaba da gudanar da bincike bayan kame maharin.

Harin dai shi ne irinsa na biyu cikin mako guda a irin shagunan zamanin, haka zalika ya zo ne bai wuce kwanaki 7 dafaruwar makamancinsa a jihar California ba.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.