Isa ga babban shafi
Duniya

Iran ta musanta harbo jirginta daga Amurka

Ministan harkokin wajen Iran Muhammad Javad Zarif ya ce babu gaskiya cikin ikirarin da Amurka ta yi na harbo wani jirgin leken asirinta maras matuki a mashigin ruwan Hormuz.

Mashigin ruwan Hormuz
Mashigin ruwan Hormuz Reuters
Talla

Javad Zarif ya bayyana haka ne bayan isa zauren majalisar dinkin Duniya don ganawa da babban sakatarenta Antonio Gutterresh.

A jiya Alhamis shugaban Amurka Donald Trump ya sanar da cewa dakarun kasar sun harbo jirgin leken asirin na Iran, bayan da ya ketara iyakar da ke tsakaninsu a mashigin ruwan Hormuz.

A makwannin baya Iran ta taba kakkabo irin jirgin leken asirin na Amurka maras matuki, bayan ketara kan iyakarta da tace yayi, zargin da Amurka ta musanta a wancan lokaci,tarkacen jirgin da Iran ta gabatarwa manema labaren kasar ta.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.