Farfesa Balarabe Sani Garko na Jami’ar Ahmadu Bello kan rashin yiwa miliyoyin yara rigakafin cutuka
Wallafawa ranar:
Kunna - 03:26
Majalisar Dinkin Duniya ta bayyana cewar akalla yara miliyan 20 a fadin duniya ba a iya yiwa rigakafin kamuwa da cututtuka ba a shekarar da ta gabata, yayin da karuwar masu kamuwa da cutar kyanda yanzu haka ke haifar da fargaba.Rahotan shekara shekara da Hukumar Lafiya ta Majalisar da kuma na Hukumar UNICEF suka gabatar, sun ce yara kusan miliyan 19 da rabi ne basu samu rigakafin ba, adadin da ya dara na shekarar 2017 inda aka samu sama da miliyan 18 da rabi.Dangane da wannan da kuma illar da ke iya janyowa yara, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Farfesa Balarabe Sani Garko na Jami’ar Ahmadu Bello.