Isa ga babban shafi
Turkiya

Na'urar kakkabo makamai da Rasha ta kerawa Turkiya sun isa hannunta

Shugaban kasar Turkiya Recep Tayyip Erdogan ya bayyana farin cikin sa da samun na’urorin kakkabo makamai masu linzami daga Rasha, duk da adawar da Amurka keyi da cinikin.

Shugaban Turkiya Recep Tayyip Erdogan
Shugaban Turkiya Recep Tayyip Erdogan Reuters/路透社
Talla

Yayin da ya ke jawabi a ranar da kasar ta cika shekaru 3 da yunkurin juyin mulkin da bai samu nasara ba, Erdogan ya ce sun fara karbar wadannan makamai wadanda wasu ke cewa ba za su iya ba.

A watan Yulin shekarar 2016 wasu sojin kasar suka yi yunkurin kifar da gwamnatin Erdogan, abinda ya yi sanadiyar kashe akalla mutane 250, yayin da sama da 2,000 suka samu raunuka.

Kawo yanzu dai Gwamnatin Turkiya na ci gaba da kame tare da hukunta daidaikun mutanen da ke hannu ko kuma masaniya koma suka taimakawa yunkurin juyin mulkin.

Kasar Amurka dai tun bayan fara cinikin makaman tsakanin Rasha da Turkiyan ta gargadi Erdogan kan cinikin wanda ta ce barazana ne ga tsaro, baya ga yi masa barazanar karin takunkumai da kuma koro daliban Turkiyan da ke karatu can a Amurka.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.