Isa ga babban shafi
Cambodia

Mutane 24 sun mutu a rubtawar gini a Cambodia

Akalla mutane 24 sun rasa rayukansu sakamakon rubtawar wani ginin bene mai hawa bakwai a Cambodia, yayinda masu aikin agaji ke ci gaba da kokarin zakulo wadanda buraguzai suka binne duk da cewa, ana kyautata zaton babu mai sauran numfashi.

Wurin da aka samu ibtila'in rushewar gini a Cambodia
Wurin da aka samu ibtila'in rushewar gini a Cambodia Den AYUTHYEA / AFP
Talla

Rahotanni na cewa, benen da ba a kammala gininsa ba, ya rubta ne a daidai lokacin da ma’aikatan ginin da iyalansu ke barci a cikin sa.

Ana yawan samun matsalar rushewar gine-gine a Cambodia, kasar da ta yi fice wajen rashin daukan tsauraren matakai kan masu karya dokokin gine-gine.

Sai dai a wannan karo an cafke mutanen China guda uku da ke kula da ginin, kuma  a halin yanzu ana kan gudanar da bincike.

Firaministan kasar, Hun Sen ya ziyarci inda ibtila’in ya faru a yankin Sihanoukville dake kusa da gabar teku.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.