Isa ga babban shafi

Amurka za ta sake girke dakaru dubu 5 a gabas ta tsakiya

Wasu Rahotanni daga Amurka na nuna cewa ma’aikatar tsaron kasar Pentagon na shirin aikewa da Karin dakarun soji dubu 5 zuwa yankin gabas ta tsakiya dai dai lokacin da alaka ke kara tsami tsakanin Iran da kasashen yankin da ke kawance da Amurkan.

Shugaba Donald Trump tare da mai bashi shawara kan harkokin tsaro Lt. Gen. H.R. McMaster
Shugaba Donald Trump tare da mai bashi shawara kan harkokin tsaro Lt. Gen. H.R. McMaster REUTERS/Kevin Lamarque/File Photo
Talla

Matakin na Amurka na zuwa dai dai lokacin da alaka ke kara tsami tsakaninta da Iran tun bayan daura aniyar dakatar da Tehran daga fitar da albarkatun manta zuwa kasuwannin duniya.

Wasu manyan hafsoshin sojin Amurka da ke shalkwatar tsaron kasar, sun bayyana cewa, cibiyar gudanar da ayyukan soji da kanta ce ta bukaci ma’aikatar da Pentagon da aike da tarin dakarun dubu 5 ga gabas ta tsakiya, sai majiyar ta ce kawo yanzu Pentagon ba ta nuna amincewa da bukatar ba.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.