Isa ga babban shafi
Isra'ila-Falasdinawa

Isra'ila ta janyewa Falasdinawa dokar hana kamun kifi

Isra’ila ta janye dokar haramcin kamun kifi da ta kakabawa, kananan jiragen ruwan Falasdinawa da ke sana’ar suu a gabar ruwan da ke kan iyakarta da yankin Gaza.

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu
Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu Abir Sultan/Pool via REUTERS
Talla

Matakin dage haramcin kamun kifin, wani bangare ne na soma aiwatar da yarjejeniyar tsagaita wutar da bangarorin suka cimma, bayan da a makon da ya gabata, Jiragen yakin Isra’ila suka kai wa cibiyoyin mayakan kungiyar Islamic Jihad da ke gaza farmaki, a matsayin martini kan harba makaman roka akalla 250 da suka yi cikin Isra’ilar.

A baya dai sojin ruwan Isra’ila kan bude wuta kan Falasdinawan da ke sana’ar ta ta kamun kifi a duk lokacin da suka ketara kan iyakar ruwan da ke tsakaninsu.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.