Isa ga babban shafi
Saudiya

Saudiya na kashe 'Yan Shi'a a kasar- Amnesty

Kungiyoyin Kare Hakkin Bil'adama na duniya da suka hada da Human Rights Watch da Amnesty International sun yi zargin cewar, 33 daga cikin mutane 37 da Saudi Arabia ta aiwatarwa da  hukuncin kisa, mabiya akidar Sh'ia ne.

Majalisar Dinkin Duniya ta bukaci Saudiya da ta sauya dokokinta na aiwatar da hukuncin kisa
Majalisar Dinkin Duniya ta bukaci Saudiya da ta sauya dokokinta na aiwatar da hukuncin kisa IRAQ JUSTICE MINISTER / AFP
Talla

Adam Coogle na Kungiyar Human Rights Watch ya yi zargin cewar, shari’ar da aka yi wa wadannan mutane bata da inganci, yayinda Daraktar Amnesty International a Gabas ta Tsakiya, Lynn Maalouf ta ce, wannan ya nuna yadda ake amfani da hukuncin kisa saboda siyasa.

Kakakin Hukumar Kare Hakkin Bil'adama ta Majalisar Dinkin Duniya, Ravina Shamdasani ta ce, suna  kira ga gwamnatin Saudi Arabia da ta sake duba wadannan shari’u, musamman wasu guda uku daga cikinsu.

Jami'ar ta ce, suna da labarin cewar, wasu daga cikin wadanda aka aiwatar da hukuncin kisan, yara ne kanana 'yan kasa da shekaru 18.

A cewar Shamdasani, dokokin duniya sun haramta kashe kananan yara. yayinda ta ce, rahotannin da suka samu sun nuna musu cewa, wadanda aka kashe sun aikata laifin shiga zanga-zangar adawa da gwamnatin kasar  ne.

Kodayake jami'ar ta ce, hukuncin da aka yanke wa wadannan mutane ya yi daidai da dokar yaki da ta’addanci a  Saudiya, amma ta ce, suna kira ga mahukuntan kasar da su sake nazari kan dokar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.