Isa ga babban shafi
Amnesty

An samu raguwar yanke hukuncin kisa a Duniya- Amnesty

Wani rahoton kungiyar kare hakkin bil adama ta Amnesty ya ce aiwatar da hukuncin kisa a fadin duniya ya ragu ainun, fiye da yadda lamarin ya ke a shekaru goma da suka wuce, yayin da a wasu daidaikun kasashe an samu karuwar irin wannan hukunci da kuma aiwatar da shi.

Tambarin kungiyar kare hakkin dan adam ta Amnesty International
Tambarin kungiyar kare hakkin dan adam ta Amnesty International Amnesty
Talla

Rahoton da kungiyar kare hakkin bil adama na Amnesty ta fitar a ranar Laraba na nuni da cewa, batun aiwatar da hukuncin kisa a Iran ya ragu matuka da kashi 50 cikin dari, biyo bayan sauye sauyen da ta gudanar a dokokinta kan muggan kwayoyi, haka ma lamarin ya ke a Iraqi, Pakistan da Somalia.

Rahoton ya ci gaba da cewa hukuncin kisa, tare da aiwatar da shi ya karu a kasashen Belarus, Japan, Singapore da Sudan ta kudu da Amurka, yayin da Thailand ta dawo da aiwatar da hukuncin a karon farko cikin shekaru goma, sai kuma Sirilanka da ke barazanar bin sahun Thailand.

An samu ci gaba kamar yadda rahoton ya nuna, inda jimilla, yawan hukuncin kisa ya fadi a fadin duniya, daga 993 a shekarar 2017, zuwa akalla 690 a shekarar da ta gabata.

Wannan alkaluma da kungiyar ta Amnesty ta fitar babu ta China a ciki, wacce duk duniya babu kasar da ta kai ta aiwatar da hukuncin kisa, inda ake boye adadin a matsayin wani babban sirri na kasa, kungiyar ta kiyasta cewa dubban mutane ne ake yanke wa hukuncin kisa kuma ake aiwatar da shi duk shekara a China.

Wannan nazari na shekara shekara da kungiyar ta Amnesty ta yi dai ya nuna cewa kokarin da ake na hana yanke hukuncin kisa da aiwatar da shi a duniya ya na samun goyon baya, duba da yadda wasu kasashe suka bi sawun masu soke hukuncin kisa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.