Trump zai gana da Kim a birnin Hanoi na Vietnam
Shugaban Amurka Donald Trump ya sanar da birnin Hanoi na kasar Vietnam a matsayin wurin da zai gana da shugaban Korea ta Arewa Kim Jong Un ranar 27 zuwa 28 ga watan nan.
Wallafawa ranar:
Ganawar shugabannin biyu nan da 'yan kwanaki ana saran za ta mayar da hankali kan matakan da Korea ta arewa ke bi wajen kawo karshen shirinta na nukiliya baya ga lalata makaman da ta mallaka.
Cikin sakon da Donald Trump ya wallafa a shafinsa na Twitter ya ce tuni jami’ansa na musamman suka gana da jami’an Korea game da ganawar kuma tuni suka amince da wuri da lokaci.
A watan Yinin bara ne Donald Trump ya yi ganawa ta farko da Kim Jong Un a Singapore, ganawar da ta kawo akrshen musayar zafafan kalamai tsakanin shugabannin biyu masu tsohuwar gaba.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu