Alhaji Sulaiman Garba Krako Saminaka kan matakin Amurka na neman kasashe su rika biyanta kafin basu tsaro
Wallafawa ranar:
Kunna - 03:35
Shugaban Amurka Donald Trump ya sanar da aniyar kasar ta kawo karshen rawar da ta ke takawa a matsayin ‘yan sandar duniya, in da ya ke cewa, akwai bukatar kasashe su biya kudade kafin Amurkan ta ba su tsaro.Trump ya bayyana haka ne a yayin ziyarar ba-zata da ya kai wa dakarun Amurka da ke Iraqi, kuma ya bayar da tabbacin cewa, ba zai janye dakarun ba kamar yadda ya yi a Syria. Sai dai tuni masharhanta kan al’amuran siyasa suka alakanta ziyarar Trump da wani yunkurin wanke kanshi daga caccakar da ake yi masa a ciki da wajen kasar, kamar yadda za ku ji karin bayani a hirar da Abdurrahman Gambo ya yi da Alh. Sulaiman Garba Krako Saminaka da ke fashin bakin siyasa a Amurka.