Saudiya ta yi watsi da bukatar binciken kasashen duniya kan Khashoggi
Ministan harkokin wajen Saudi Arabia Adel al-Jubeir ya yi watsi da bukatar Turkiya na gudanar da binciken kasashen duniya kan hallaka Dan Jarida Jamal Khashoggi.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Al-Jubeir ya ce Saudiya na da hukumomin binciken ta kuma ba za ta amince da duk wata bukatar kafa wani kwamitin kasashen duniya ba, domin yanzu haka batu ne na shari’a kuma za’a gabatar da wadanda ake zargi su 5 a gaban kotu domin amsa tambayoyi.
Hukumomin Turkiya sun bayyana shaku kan rahotan binciken da Saudiya ta gabatar wanda ya nesanta Muhammad bin Salman daga zargin ba da umurnin kashe dan jaridar.
Ministan harkokin wajen Turkiya Mevlut Cavusoglu ya ce babu wani sabon abu da rahotan binciken Saudiya yayi bayani, banda tabbatar da abinda suka sani na kasha Khashoggi da kuma narkar da gawar sa.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu