Hamas ta sanar da tsagaita wuta da Isra'ila
Kungiyar Hamas ta Falasdinawa ta sanar da kulla yarjejeniyar tsagaita wuta da Isra’ila wadda kasar Masar ta shiga tsakanin bayan kwashe kwana biyu ana fafatawa a tsakanin su.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
A yankin,Falasdinawa sun harba makaman roka akalla 460 cikin Israila a cikin kwanaki biyu, abinda ba’a taba gani ba, wanda ya raunana Yahudawa 27, yayin da Israila ta mayar da martani da hare haren sama a wuraren da tace mallakar kungiyar Hamas ne da Islamic Jihad.
Majalisar Dinkin Duniya ta gudanar da taro a asirce amma babu wani bayani da akayi a kai.
Jakadan Falasdinawa a Majalisar Dinkin Duniya Riyad Mansour ya bukaci kwamitin sulhu ya dauki nauyin da ya rataya akan ta.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu