Isa ga babban shafi
Amurka

Trump ya kori Ministan Shari'ar Amurka

Shugaban Amurka Donald Trump ya kori Ministan Shari’arsa Jeff Sessions, kwana guda da gudanar da zaben tsakiyar wa’adi, in da jam’iyyar Republican mai mulki ta rasa rinjaye a zauren Majalisar Wakilai.

Jeff Sessions tare da Donal Trump wajen yakin neman zaben 2016
Jeff Sessions tare da Donal Trump wajen yakin neman zaben 2016 REUTERS/Marvin Gentry/File Photo
Talla

A wani sakon Twitter da ya aika, shugaba Trump ya mika godiya ga Sessions kan gudunmawar da ya bayar tare da yi masa fatan alheri.

Shugaba Trump ya sha caccakar tsohon Ministan Shari’ar bayan ya tsame kansa daga binciken da ake gudanarwa kan zargin Rasha da yin katsalandan a zaben Amurka na 2016.

Trump ya ce, shugaban ma’aikata a ofishin Sessions, Mathew Whitaker wanda ya sha sukar binciken kutsan Rashan, zai maye gurbin Ministan Shari’a na rikon kwarya.

Ana ganin wannan matakin na Trump zai kara janyo cece-kuce game da makomar binciken kutsan zaben, in da wasu ke zargin cewa, fadar White House na kokarin kashe maganar binciken ne baki daya.

A bangare guda, ana hasashen cewa, akwai yiwuwar Trump ya yi garambawul a Majalisar Ministocinsa bayan kammala zaben na tsakiyar wa’adi.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.